ข้ามไปยังเนื้อหา
Ƙidaya 16:45-48

Ƙidaya 16:45-48

45
“Ku nisanci wannan taro, gama yanzu nan zan hallaka su.” Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki.
46
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki farantinka ka sa turare a ciki, da wuta daga bagade, ka yi maza ka tafi wajen taron, ka yi kafara dominsu. Gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko; an kuma fara annoba.”
47
Saboda haka Haruna ya yi kamar yadda Musa ya faɗa, ya ruga a guje zuwa tsakiyar taron. An riga an fara annobar a cikin mutane, amma Haruna ya miƙa turaren ya kuma yi kafara dominsu.
48
Ya tsaya tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options