Nehemiya 5:6-7
6
Sa’ad da na ji kukansu da waɗannan koke-koke, na husata ƙwarai.
7
Na yi tunaninsu a zuciyata sa’an nan na zargi manyan gari da shugabanni. Na ce musu, “Kuna musguna wa ’yan’uwanku ta wurin ba su rance da ruwa!” Saboda haka na kira babban taro gaba ɗaya don a magance wannan.