Skip to content
Mattiyu 27:50-51

Mattiyu 27:50-51

50
Da Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sai ya saki ruhunsa.

Mutuwar Yesu da abin da ya biyo baya

51
A daidai wannan lokaci, sai labulen haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta jijjiga, duwatsu kuma suka farfashe.

Duba kuma

Sauran wuraren da Nassi ya faɗi haka

  • Ibraniyawa 10:19

    Saboda haka, ’yan’uwa, da yake muna da wannan tabbaci na shiga Wuri Mafi Tsarki ta wurin jinin Yesu,
    daga aya ta 51
  • Ibraniyawa 10:22

    bari mu matso kusa da Allah da zuciya mai gaskiya da kuma cikakken tabbaci mai zuwa ta wurin bangaskiya. Bari mu bar zukatan da tsabta, lamirinmu babu mugunta, da kuma jikunanmu a wanke da ruwa.
    daga aya ta 51
  • Markus 15:38

    Labulen haikali kuwa ya yage kashi biyu, daga sama har ƙasa.
    daga aya ta 51
  • Ibraniyawa 6:19

    Muna da wannan bege kamar anka na rai, kafaffe da kuma tabbatacce. Yana shiga tsattsarkan wuri na can ciki a bayan labule,
    daga aya ta 51
  • Luka 23:45

    domin rana ta daina haskakawa. Labulen da yake cikin haikali kuma ya yage kashi biyu.
    daga aya ta 51
  • Ru’uya ta Yohanna 11:19

    Sa’an nan aka buɗe haikalin Allah da yake a sama, kuma a cikin haikalinsa aka ga akwatin alkawarinsa. Sai kuwa ga walƙiya, ƙararraki, tsawa, girgizar ƙasa, da kuma ƙanƙara masu girma.
    daga aya ta 51
  • Fitowa 26:31

    “Ka yi labule mai ruwan shuɗi, shunayya da jan zare da kuma lallausan lilin da aka tuƙa, da zānen kerubobin da mai fasaha ya yi.
    daga aya ta 51
  • Fitowa 26:37

    Ka yi ƙugiyoyin zinariya domin wannan labule da katakai itacen ƙirya biyar, waɗanda aka dalaye da zinariya. Ka kuma yi zubi na tagulla biyar dominsu.
    daga aya ta 51
  • Yohanna 19:30

    Da ya tsotsi abin sha ɗin, sai Yesu ya ce, “An gama.” Da wannan fa, ya sunkuyar da kansa ya saki ruhunsa.
    daga aya ta 50
  • Mattiyu 27:54

    Da jarumin nan tare da waɗanda suke tsaron Yesu, suka ga girgizar ƙasa, da kuma abin da ya faru, sai tsoro ya kama su, suka kuma ce, “Gaskiya, wannan Ɗan Allah ne!”
    daga aya ta 51
  • Ishaya 53:9

    Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
    daga aya ta 50
  • Ishaya 53:12

    Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.
    daga aya ta 50

Inda wannan ya faru

All Matthew Sites (Jerusalem)
All Matthew Sites (Jerusalem) View full PDF
Matthew 27:45-55
Matthew 27:45-55 View full PDF
The Last Week of Jesus' Life (With Reference Table)
The Last Week of Jesus' Life (With Reference Table) View full PDF

Map © Biblica Open Bible Maps · CC BY-SA 4.0

Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options