Mattiyu 21:37-39
37
A ƙarshe, sai ya aiki ɗansa a wurinsu. Ya ce, ‘Za su girmama ɗana.’
38
“Amma da ’yan hayan suka hangi ɗan, sai suka ce wa juna, ‘Wannan shi ne magājin. Ku zo, mu kashe shi, mu ci gādonsa.’
39
Saboda haka suka kama shi, suka jefar da shi bayan katangar gonar inabin, suka kashe shi.