Mattiyu 17:14-16
14
Da suka isa wajen taron, sai wani mutum ya zo ya durƙusa a gabansa.
15
Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
16
Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”