Skip to content
Mattiyu 15:34-38

Mattiyu 15:34-38

34
Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?” Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da ’yan ƙananan kifaye.”
35
Ya sa taron su zazzauna a ƙasa.
36
Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane.
37
Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai.
38
Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options