Mattiyu 14:15-18
15
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
16
Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
17
Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
18
Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
Settings