Markus 15:17-19
17
Suka sa masa wata riga mai ruwan shunayya, suka kuma tuƙa rawanin ƙaya suka sa masa.
18
Sai suka fara ce masa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
19
Suka dinga bugunsa a kā da sanda, suka tattofa masa miyau. Suka durƙusa suka yi masa bangirma na ba’a.