Luka 7:47-50
47
“Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawa, an gafarta mata, gama ƙaunarta mai yawa ce. Amma wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, yakan nuna ƙauna kaɗan.”
48
Sai Yesu ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.”
49
Sauran baƙin suka fara ce wa juna, “Wane ne wannan, wanda har yake gafarta zunubai?”
50
Yesu ya ce wa macen, “Bangaskiyarki ta cece ki, ki sauka lafiya.”
Settings