Luka 20:37-38
37
Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
38
Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”