Luka 20:34-36
34
Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure,
35
amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba.
36
Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su ’ya’yan Allah ne, tun da su ’ya’yan tashin matattu ne.
Settings