Luka 1:8-13
8
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
Settings