Skip to content
Luka 1:12

Luka 1:12

Ana nuna aya 12 tare da mahallin da ke kewaye.
9
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options