Skip to content
Firistoci 26:27-33

Firistoci 26:27-33

27
“ ‘In duk da haka kuka ci gaba da ƙin saurare ni, kuka ci gaba da yin adawa da ni,
28
cikin fushina, sai in yi adawa da ku, in kuma hukunta ku saboda zunubanku har sau bakwai.
29
Za ku ci naman ’ya’yanku maza da na ’ya’yanku mata.
30
Zan rurrushe dukan masujadanku, in yanke bagadanku na turare, in yi tarin gawawwakinku a kan gumakanku, zan kuma yi ƙyamarku.
31
Zan mai da biranenku kango, in lalace wuraren tsarkinku, ba zan kuma shaƙi ƙanshi hadayunku ba.
32
Zan mai da ƙasarku kango har abokan gābanku da suke zama a wurin su yi mamaki.
33
Zan watsar da ku cikin al’ummai, in kuma ja takobina in kore ku. Ƙasarku za tă zama kufai, biranenku kuma su zama kango.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options