Firistoci 24:17-21
17
“ ‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
18
Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
19
Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
20
karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
21
Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Settings