Skip to content
Firistoci 20:1

Gabatarwa ga Dokokin Laifuffuka Masu Hukuncin Kisa

Firistoci 20:1
Ana nuna aya 1 tare da mahallin da ke kewaye.
1
Ubangiji ya ce wa Musa,
2
“Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikin Isra’ila da ya miƙa wani daga cikin ’ya’yansa wa Molek, dole sa kashe shi. Mutanen ƙasar za su jajjefe shi.
3
Zan yi gāba da wannan mutum, zan kuma raba shi da mutanensa; gama ta wurin miƙa ’ya’yansa ga Molek, ya ƙazantar da wuri mai tsarkina, ya kuma ƙazantar da sunana mai tsarki.
4
In mutanen ƙasar suka kau da idanunsu sa’ad da wannan mutum ya miƙa ’ya’yansa ga Molek, suka kāsa kashe shi,
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options