Skip to content
Firistoci 16:23-25

Firistoci 16:23-25

23
“Sa’an nan Haruna zai shiga Tentin Sujada yă tuɓe rigunansa na lilin da ya sa, kafin yă shiga Wuri Mafi Tsarki, zai kuma bar su a can.
24
Zai yi wanka a tsattsarkan wuri yă sa rigunarsa na kullum. Sa’an nan zai fita yă miƙa hadaya ta ƙonawa domin kansa da hadaya ta ƙonawa domin mutane, don yă yi kafara domin kansa da kuma domin mutane.
25
Zai kuma ƙone kitsen hadaya don zunubi a kan bagade.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options