Skip to content
Mahukunta 3:12-14

Mahukunta 3:12-14

12
Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda sun aikata wannan mugunta sai Ubangiji ya ba wa Eglon sarkin Mowab ƙarfi a kan Isra’ila.
13
Da ya sami Ammonawa da Amalekawa suka haɗa hannu tare, sai Eglon ya tafi ya auka wa Isra’ila, suka ƙwace Birnin Dabino.
14
Isra’ilawa suka zama bayin Eglon sarkin Mowab shekara goma sha takwas.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options