Yohanna 5:39-47
39
Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina,
40
duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
41
“Ni ba na neman yabon mutane,
42
na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
43
Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
44
Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
45
“Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
46
Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
47
Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”
Settings