Skip to content
Yohanna 5:1-9

Yohanna 5:1-9

1
Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
2
To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
3
A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
5
Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
6
Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
7
Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
8
Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
9
Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options