23
To, yayinda yake a Urushalima a Bikin Ƙetarewa, mutane da yawa suka ga abubuwan banmamakin da yake aikata suka kuma gaskata da sunansa.
24
Sai dai Yesu bai amince da su ba, don ya san dukan mutane.
25
Ba ya bukatar shaidar mutum game da mutum, don yă san abin da yake cikin zuciyar mutum.