Skip to content
Yohanna 10:1-6

Yohanna 10:1-6

1
“Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma.
2
Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne.
3
Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje.
4
Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa.
5
Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.”
6
Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options