Ayuba 42:1-3
1
Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
2
“Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
3
Ka yi tambaya, ‘Wane ne wannan da ya ƙi karɓar shawarata shi marar ilimi?’ Ba shakka na yi magana game da abubuwan da ban gane ba, abubuwan ban al’ajabi da sun fi ƙarfin ganewata.