Ayuba 4:2-6
2
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Settings