Skip to content
Ayuba 38:1-7

Ayuba 38:1-7

1
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options