Ayuba 34:21-27
21
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
Settings