Ayuba 33:14-22
14
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da ’yan aikan mutuwa.
Settings