Ayuba 31:24-28
24
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
Settings