Ir al contenido
Ayuba 28:23-28

Ayuba 28:23-28

23
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’ ”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options