Ayuba 14:13-17
13
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni!
14
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
Settings