Skip to content
Ayuba 11:1-6

Ayuba 11:1-6

1
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options