Ayuba 10:1-3
1
“Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
2
Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
3
Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
Settings