Ayuba 10:1-7
1
“Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
2
Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
3
Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
4
Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
5
Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
6
da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
7
Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
Settings