Irmiya 52:4-5
4
A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, Sarkin Yahuda, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina katanga kewaye da ita.
5
An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
Settings