মূল বিষয়বস্তুতে যান
Irmiya 32:37-40

Irmiya 32:37-40

37
tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
38
Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
39
Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin ’ya’yansu a bayansu.
40
Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options