Ishaya 9:8-10
8
Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
9
Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
10
“Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”