Ishaya 63:2-3
2
Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka ’ya’yan inabi?
3
“Na tattake ’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.