Ishaya 6:11-12
11
Sa’an nan na ce, “Har yaushe, ya Ubangiji?” Ya kuma amsa, “Sai an lalatar da biranen ba kowa a ciki, sai an mai da gidaje kangwaye ƙasa kuma ta zama kango ba amfani,
12
sai lokacin da Ubangiji ya kori kowa aka kuma yashe ƙasar gaba ɗaya.