Skip to content
Ishaya 53:1-3

Ishaya 53:1-3

1
Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
2
Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
3
Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options