Skip to content
Ishaya 3:16-24

Ishaya 3:16-24

16
Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
17
Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
18
A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
19
’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
20
kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
21
da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
22
tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
23
da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
24
A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options