Skip to content
Ishaya 27:1

Ishaya 27:1

Ana nuna aya 1 tare da mahallin da ke kewaye.
1
A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
2
A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da ’ya’ya ku ce
3
Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
4
Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options