Ibraniyawa 11:14-16
14
Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
15
Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
16
A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
Settings