Farawa 30:9-13
9
Sa’ad da Liyatu ta ga cewa ta daina haihuwa, sai ta ɗauki mai hidimarta Zilfa ta ba da ita ga Yaƙub tă zama matarsa.
10
Baranyar Liyatu, Zilfa ta haifa wa Yaƙub ɗa.
11
Sai Liyatu ta ce, “Na yi sa’a!” Saboda haka ta ba shi suna Gad.
12
Zilfa baranyar Liyatu ta haifa wa Yaƙub ɗa na biyu.
13
Sai Liyatu ta ce, “Ni mai farin ciki ce! Mata za su ce da ni mai farin ciki.” Saboda haka ta sa masa suna Asher.
Settings