Skip to content
Farawa 27:1-4

Farawa 27:1-4

1
Sa’ad da Ishaku ya tsufa idanunsa suka raunana har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa ya ce masa, “Ɗana.” Isuwa kuwa ya amsa, ya ce “Ga ni.”
2
Ishaku ya ce, “Yanzu na tsufa kuma ban san ranar mutuwata ba.
3
Saboda haka yanzu, ka ɗauki makamanka, kwari da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama.
4
Ka shirya mini irin abinci mai daɗin da nake so, ka kawo mini in ci, domin in sa maka albarka kafin in mutu.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options