Farawa 25:1-4
1
Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
2
Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
3
Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
4
’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
Settings