Farawa 25:1-6
1
Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
2
Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
3
Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
4
’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
5
Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.
6
Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa ’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.
Settings