Galatiyawa 4:26-27
26
Amma Urushalimar da take sama ’yantacciya ce, ita ce kuma mahaifiyarmu.
27
Gama a rubuce yake cewa, “Ki yi farin ciki, ya ke bakararriya, wadda ba ta haihuwa ki ɓarke da murna, ki kuma tā da murya, ke da ba kya naƙuda; domin da yawa ne ’ya’yan macen da aka yashe, fiye da na mai miji.”