Skip to content
Ezra 5:3-5

Jami’an Farisa Sun Kalubalanci Aikin

Ezra 5:3-5
3
A wannan lokaci, Tattenai gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu suka je wurinsu suka tambaye su cewa, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali har ku gyara katangar?”
4
Suka kuma tambaye su “Ina sunayen waɗanda suke wannan gini?”
5
Amma Allah yana tsaron dattawan Yahudawa, saboda haka ba a hana su aikin ba har sai rahoto ya kai wurin Dariyus aka kuma sami amsarsa a rubuce tukuna.
Settings

Reading style

Typeface

Font size 19px

Reading width 90 chars

Options