Skip to content
Ezekiyel 11:4-7

Ezekiyel 11:4-7

4
Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
5
Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
6
Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
7
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options