Fitowa 32:3-4
3
Saboda haka dukan mutane suka tuttuɓe ’yan kunnensu suka kawo wa Haruna.
4
Sai ya karɓi abubuwan da suka ba shi, ya yi gunki na siffar ɗan maraƙi, ya sassaƙa shi da kayan aiki. Sa’ad da mutane suka gani, sai suka tā da murya suka ce, “Waɗannan su ne allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga Masar.”
Settings